in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin kasar Sin na kara kokarin yin rigakafi da ba da jiyya kan cutar murar tsuntsaye nau'in H7N9
2013-04-06 16:53:08 cri
Ya zuwa yammacin ranar Jumma'a 5 ga wata da misalin karfe 5, baki daya mutane 16 ne suka kamu da cutar murar tsuntsaye nau'in H7N9 a babban yankin kasar Sin, cikinsu kuma guda 6 sun riga sun mutu. A kwanan baya, babban sakataren kwamitin tsakiya na Jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin Xi Jinping, da firaministan kasar Li Keqiang, sun ba da umurnin kara kokarin yin rigakafi da ba da jiyya kan wannan cuta.

Kwamitin kiwon lafiya da shirin kayyade haihuwa na kasar Sin ya bayyana cewa, an riga an dauki matakan sa ido kan duk wadanda suka taba yin mu'ammala da wadanda suka kamu da cutar, a cikinsu kuma, an samu mutum guda daya da ya nuna alamar kamuwa da mura, amma ba ta murar tsuntsaye nau'in H7N9 ba, yayinda sauran suke cikin lafiya.

Kawo yanzu, cutar tana ci gaba da yaduwa, amma han yanzu ba wanda ya kamu da ita ta hanyar samun yaduwa daga mutum zuwa mutum ba.

A cikin 'yan kwanakin da suka wuce, yawan mutanen da suka kamu da cutar murar tsuntsaye nau'in H7N9 ya karu. A sabili da haka, ake kara kokarin yin rigakafi da ba da jiyya kan wannan cuta a wurare daban daban na kasar Sin.

Daga ranar Asabar 6 ga wata, za a dakatar da sayar da tsuntsaye masu rai a birnin Shanghai, tare da rufe kasuwannin sayar da tsuntsaye.

A sa'i daya, an riga an dauki kwararran matakai a birnin Beijing, lardunan Guangdong, Yunnan, Hubei, Sichuan da sauransu, inda ba a samu wadanda suka kamu da cutar ba tukuna, domin kara karfin yin rigakafi.

Gwamnatocin mataki-mataki da yawa sun yi alkawari ga kafofin yada labaru cewa, ko kadan ba za su boye labari dangane da cutar ba. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China