in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar LAS ta ba da iznin shigar dakaru masu adawa da gwamnatin kasar Syria ba bisa doka ba, in ji shugaban kasar
2013-04-06 16:50:16 cri
A daren ranar Jumma'a 5 ga wata, wani gidan talibijin mai zaman kansa na Syria ya gabatar da wani shirin intabiyu da aka yiwa shugaban kasar, Bashar al-Assad, inda ya furta cewa, kungiyar kasashen Larabawa (LAS) ta ba da iznin shigowar kungiyar adawa da gwamnatin kasar Syria cikin kungiyar ba bisa doka ba.

Game da wannan batu da kungiyar LAS ta yi a ranar 26 ga watan Maris, a kwanan baya, yayin da yake magana da kafofin yada labaru na Turkiya, Bashar al-Assad ya yi nunin cewa, a hakika , matakin da aka dauka ba shi da wani tushe a fannin doka.

A cewar shugaban,kungiyar tana wakiltar kasashen Larabawa ne, a maimakon Larabawa, kuma Kungiyar LAS, bisa doka, ba ta da ikon bayarwa ko kuma kwace ikon wata kungiya.

Bugu da kari, Bashar al-Assad ya yi gargadin cewa, idan an yi juyin juya hali ko kawo baraka ga kasar Syria,hakan zai kawo babbar illa ga tsaron shiyya-shiyya, kuma za a shiga yanayin rashin tabbas a kasashe makwabtanta, da ma yankin Gabas ta Tsakiya baki daya har na tsawon sama da shekaru 10 masu zuwa.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China