in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin tana fatan yin hadin gwiwa da kasashen Larabawa don warware batun Siriya ta hanyar siyasa
2013-04-05 17:03:53 cri
A ranar 4 ga wata, a birnin Doha hedkwatar kasar Qatar, yayin da manzon musamman game da batun Gabas ta tsakiya Wu Sike ke zantawa da wakilinmu, ya bayyana cewa, kasar Sin tana fatan yin hadin gwiwa tare da kasashen kwamitin hadin kan kasashen Larabawa na tekun Gulf, da na kungiyar hadin kan kasashen Larabawa ta AL, don suyi kokari tare, wajen warware batun kasar Siriya ta hanyar siyasa.

Wu Sike ya ci gaba da cewa, batun kasar Siriya ya zamo abin da bangarori daban daban ke dora muhimmanci sosai a kai, kuma kasar Sin kullum take tsaye kan ra'ayin warware batun ta hanyar yin shawarwari, ba wai a warware wannan batu ta hanyar karfin soji ko yin shisshigi wa kasar ba.

A sa'i daya kuma, ya ce, a halin da ake ciki yanzu, da wuya ne, a warware batun kasar Siriya ta hanyar siyasa, amma wannan ba wai yana nufin cewa za a yi watsi da wannan hanya ba ne.

kasar Sin za ta dage wajen nuna goyon baya ga rawar da M.D.D. da kungiyar AL suke takawa wajen warware batun Siriya. Haka kuma, Mr. Wu ya jaddada cewa, kasar Sin ba za ta nuna goyon baya ko kuma yin adawa da ko wane bangare ba, kuma za ta yi la'akari ne da moriyar jama'ar kasar Siriya, don sa kaimi ga warware batun ta hanyar siyasa.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China