in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gano mutane 4 da suka kamu da murar tsuntsaye nau'in H7N9 a jihar Jiangsu ta kasar Sin
2013-04-03 13:43:37 cri
Bisa sanarwar da hukumar kula da kiwon lafiya da kayyade haihuwa ta kasar Sin ta bayar a ranar 2 ga wata, an ce, an gano mutane 4 da suka kamu da murar tsuntsaye nau'in H7N9 a jihar Jiangsu ta kasar, wadanda a yanzu haka ake kokarin yi musu jiyya..

Bisa labarin da aka bayar, an ce, daya daga cikin mutanen hudu mai aikin fidan kaza ne, kuma dukkan mutanen 4 da suka kamu da cutar suna jin zazzabi, ciwon kai, tare kuma da yin tari.

Ya zuwa yanzu dai, ba a gano wata alaka tsakanin mutanen hudu ba dangane da yaduwar cutar, kana mutanen dake zama tare da su ba sa jin zazzabi ko kuma yin tari ya zuwa yanzu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China