in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afirka ta Kudu ta yi zaman makoki wa sojojin kasar da suka mutu a yakin kasar Afirka ta Tsakiya
2013-04-03 10:48:12 cri
A ranar 2 ga wata, kasar Afirka ta Kudu ta gudanar da zaman makoki wa sojojin kasar guda 13 da suka mutu a yakin kasar Afirka ta Tsakiya, inda shugaban kasar Jacob Zuma ya nuna yabo ga sojojin kuma a cewarsa sun rasu ne a aikin kiyaye zaman lafiya a yankin. Ya kuma musanta zargin da ake yi masa na cewa an tura sojojin kasar zuwa kasar Afirka ta Tsakiya ne domin tabbatar da moriyar jam'iyyarsa ta ANC.

Shugaba Zuma ya bayyana cewa, wadannan sojoji guda 13 sun rasa ranyukansu ne a aikin bin manufofin diplomasiyya na kasar Afirka ta Kudu da kuma kiyaye zaman lafiya a nahiyar Afirka, don haka ya kamata kasarsu ta nuna yabo gare su.

A watan Janairu na shekarar bana, kasar Afirka ta Kudu ta tura sojoji guda 200 zuwa kasar Afirka ta Tsakiya don taimakawa sojojin gwamnatin kasar wajen yaki da dakaru masu adawa.

A kuma ranar 24 ga watan Maris, dakaru masu adawa a kasar Afirka ta Tsakiya sun mamaye babban birnin kasar, inda sojojin kasar Afirka ta Kudu 13 suka mutu a sakamakon musayar wuta, kana sojoji fiye da 20 suka ji rauni. Wannan shi ne karo na farko da kasar Afirka ta kudu tayi asarar sojoji da suka kai hakan yawa a cikin shekaru 20 da suka gabata. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China