in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kafofin yada labaru na Amurka sun mai da hankali game da ziyarar farko ta shugaban kasar Sin
2013-04-01 11:20:42 cri
Ziyarar farko da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi bayan da ya hau karagar mukami, ba ma kawai ta samu karbuwa daga shugabanni da jama'ar kasashen da ya ziyarta ba ne, har ma ta yi matukar jawo hankalin kafofin yada labaru na kasashen waje.

A yayin ziyarar, kafofin yada labaru na kasar Amurka irinsu, jaridar "The New York Times" sun rubuta bayani da cewa, a yayin ziyarar farko ta shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi bayan hayewarsa karagar mukami, ya yi sharhi game da burin kasar Sin, da batun tattalin arziki da cinikayya, da dangantakar da ke tsakaninta da manyan kasashen da suke samun bunkasuwa sosai. Bayanin ya ruwaito wani kwararren kasar Sin na cewa, daga cikin kasashen da shugaban Xi ya ziyarta, ana iya gano cewa, kasar Sin na dukufa ka'in da na'in wajen yunkurin raya batun kasa da kasa cikin demokuradiyya, da kokarta sa kaimi ga kafa tsarin dokokin kasa da kasa cikin adalci.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China