in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kafofin yada labaru na Birtaniya sun mai da hankali game da ziyarar farko ta shugaban kasar Sin
2013-04-01 11:21:09 cri
Ziyarar farko da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi bayan da ya hau karagar mukami, ba ma kawai ta samu karbuwa daga shugabanni da jama'ar kasashen da ya ziyarta ba ne, har ma ta yi matukar jawo hankalin kafofin yada labaru na kasashen waje.

Kamfanin gidan rediyon Birtaniya BBC ya yi bayanin cewa, a yayin ziyarar shugaban Xi, ya daddale yarjejeniyoyi da shugabannin kasashen duniya da dama, kuma ya ba da tabbaci game da inganta dangantakar hadin gwiwa tsakanin bangaren kasar Sin da kasashen Afrika.

A cikin 'yan shekarun nan, kasar Sin ta zama babbar abokiyar cinikayyar kasashen Afrika. A yayin ziyarar, Shugaban Xi ya bayyana cewa, tasirin bunkasuwar kasar Sin, ta zama wata babbar dama da ba a taba ganin irinta ba ga kasashen Afrika, haka kuma ita ma bunkasuwar kasashen Afrika, ta kawo alfanu ga kasar Sin, sabo da haka, Sin tana fatan yin kokari tare da kasashen Afrika, don yin amfani da wannan dama.

Kafofin yada labaru na kasar Birtaniya kamar jaridar "Financial Times" da ta "Guardian" da "The Daily Telegraph" sun rubuta bayanai da dama, don bayyana halin da ake ciki game da ziyarar shugaban kasar Sin a kasashen waje. (Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China