in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunonin sojojin Sudan da Sudan ta Kudu sun janye daga yankunan kwance damara
2013-04-01 11:09:06 cri
Ran 31 ga watan Maris, kakakin rundunar sojan kasar Sudan Saad ya sanar da cewa, sojojin kasarsa da na Sudan ta Kudu, sun riga sun janye daga yankunan kwance damara da ke iyakar kasashen biyu.

Ko da yake dai kawo yanzu, kwamitin sa ido bai gaskanta wannan lamari ba, amma an tabbatar da cewa, yanzu babu sojojin dake cikin yankunan kwance damara.

Kakakin ya jadadda cewa, ana samun kyakkyawan yanayin tsaro a iyakar kasashen biyu, bisa dalilin gudanar da yarjejeniyar tsaro tsakanin bangarorin biyu, ya kuma bayyana cewa, dole ne kasar Sudan ta Kudu ta tsayar da tuntubarta tare da 'yan tawayen kasar Sudan ta kungiyar neman 'yancin kan jama'ar kasa SPLA, wannan shi ne muhimmin mataki wajen cimma nasarar shimfida yarjejeniyar tsaro da kasashen biyu suka sanya hannu, haka shi ma ya kasance wani babban kalubale gare su. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China