in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Faransa ta yi maraba da nadin shugaban kwamitin shawarwari da neman sulhu a Mali
2013-04-01 10:12:14 cri
Ran 31 ga watan Maris, ministan harkokin wajen kasar Faransa Laurent Fabius ya sanar da cewa, kasar Faransa na matukar farin ciki, don gane da nadin shugaban kwamitin shawarwari da neman sulhu da gwamnatin kasar Mali ta yi a ranar 30 ga watan na Maris, yana mai cewa, hakan muhimmin mataki ne na cimma nasarar sulhu ta hanyar siyasa.

Mr. Fabius ya kuma bayyana cewa, zai ziyarci kasar ta Mali ran 5 ga watan Afrilun nan, don ganawa da manyan jami'an gwamnatin wucin gadin kasar Mali.

Ran 30 ga watan Maris, shugaban gwamnatin wucin gadin kasar Mali Dioncounda Traore, ya nada shugaba da kuma mataimakin shugaban kwamitin shawarwari da neman sulhun kasar. Kuma bisa shirin da gwamnatin ta gabatar, kwamitin zai kunshi mambobi 30, wadanda za su dukufa wajen nemen hanyoyin wanzar da sulhu, tsakanin bangarori daban daban da rikicin kasar ya shafa ta hanyar shawarwari. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China