in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babbar Kotun kasar Kenya ta tabbatar da nasarar zaben shugaba Kenyatta
2013-03-31 16:23:44 cri
A jiya Asabar ne babbar kotun kasar Kenya ta tabbatar da sahihancin babban zaben kasar da ya gabata, wanda ya baiwa shugaba Uhuru Kenyatta nasarar kasancewa halastaccen shugaban kasar, bayan dukkanin alkalan kotun sun cimma matsaya guda don gane da hakan.

Babban mai shari'a Dr. Wily Mutunga ne ya bayyana amincewar daukacin alkalai 6 da suka jagoranci shari'ar, yana mai cewa za a fidda cikakken kofin shari'ar nan da makwannin biyu masu zuwa. Bugu da kari mai shari'a Mutunga ya ce, lokaci yayi da al'ummar kasar, da ragowar masu fada a ji, zasu hada kai domin wanzar da yanayin zaman lafiya da kwanciyar hankali a dukkanin fadin kasar.

Kafin bayyana hukuncin da babbar kotun ta yanke, da dama daga manazarta harkokin siyasa na kallon shari'ar a matsayin irinta ta farko da aka gudanar a kasar ta Kenya, wadda ke gabashin nahiyar Afirka. Duba da cewa wannan ne karon farko da aka gudanar da shari'ar kafin rantsar da zababben shugaban kasar. (Saminu Alhassan Usman)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China