Shugaban kasar Sin, Mr.Xi Jinping ya dawo nan birnin Beijing a Lahadi 31 ga wata da safe, bayan da ya kammala ziyara a kasashen Rasha, Tanzaniya, Afirka ta kudu da kuma jamhuriyar Congo, tare da halartar taron shugabannin kasashen BRICS karo na biyar da aka gudanar a birnin Durban na kasar Afirka ta Kudu.
A ranar 30 ga wata, shugaban kasar Sin ya bar birnin Brazzaville, babban birnin kasar jamhuriyar Congo, wadda ta kasance zangon karshe a wannan ziyararsa, inda shugaban kasar ta Congo ya shirya kasataccen biki a filin jirgi, don yin ban kwana da shi.(Lubabatu)