in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane a kalla 4 sun rasa rayuka sakamakon faduwar wani ginin da ake ginawa a Tanzaniya
2013-03-30 16:32:07 cri
A ranar Jumma'a 29 ga wata da safe, a birnin Dar es Salaam, birni mafi girma a kasar Tanzaniya, wani gini mai benaye 16 da ake ginawa ya fadi ba zato ba tsammani. Ya zuwa daren wannan rana, mutane a kalla 4 sun rasa rayukansu sakamakon hadarin, yayin da wasu 60 suka bace, ba a gano su cikin baraguzan ginin ba tukuna.

Kafofin yada labaru na wurin suna ganin cewa, sakamakon kokarin kammala ginawa gine-gine cikin sauri wato kafin lokacin da aka tsai da shi ne ya sa ba a sa ido yadda ya kamata kan wasu gine-gine a lokacin da ake gina su, ta haka gine-ginen ba su da inganci sosai, inda lamarin da ya haifar da irin wannan hadari. Kafin wannan lamari na yanzu, an samu hadarurrukan faduwar gine-gine a Dar es Salaam. (Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China