in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar IOC ta yi nazari kan birnin Istanbul na kasar Turkiya, dake neman samun iznin gudanar da wasannin Olympics na shekarar 2020
2013-03-29 18:52:15 cri
A kwanakin baya, hukumar kula da harkokin wasannin Olympics ta duniya wato IOC, ta tura wata tawaga zuwa birnin Istanbul dake kasar Turkiya, don yin nazari na kwanaki hudu. A halin yanzu, birnin Istanbul na yin takara tare da biranen Tokyo, da Madrid na kasar Sifaniya, wajen neman samun iznin gudanar da wasannin Olympics na shekarar 2020.

Tawagar hukumar IOC ta bar birnin na Istanbul a daren ranar 23 ga wata, bayan da ta kammala bincike a Tokyo da Madrid. Shugaban kasar Turkiya Abdullah Gul, ya halarci taron bayyana halin da birnin na Istanbul ke ciki, don gane da daukar nauyin shirya wasannin na Olympics, tare da jami'an hukumar kula da harkokin wasannin Olympics na kasar Turkiyan, inda suka nemi goyon baya daga tawagar hukumar ta IOC. Shugaba Gul ya bayyana cewa, idan aka cimma nasarar gudanar da wasannin a birnin Istanbul, hakan zai zama karo na farko na gudanar wasannin na Olympics a nahiyoyi biyu.

Wannan ne karo na biyar da birnin Istanbul ya yi kokarin neman samun iznin gudanar da wasannin na Olympics, inda a baya har karo hudu ya gaza cimma nasarar hakan. Za a gabatar da sakamakon ne dai na wannan karo, a watan Satumbar dake tafe a kasar Argentina.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China