in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jama'a'yan kabilu daban daban dake birnin Lhasa sun yi bikin cika shekaru 54 da aka 'yantar da miliyoyin bayi manoma da makiyaya a Tibet
2013-03-28 17:05:36 cri
A ranar 26 ga wata, wakilai na kabilu da na sassa daban daban na birnin Lhasa, sun yi taron tattaunawa don tunawa da ranar cika shekaru 54 da aka 'yantar da miliyoyin bayi manoma da makiyaya a jihar Tibet da ke kasar Sin, haka kuma mahalartan taron sun yi waiwaye adon tafiya, tare da karfafa zukatansu, da hagen nesa game da makomar samun bunkasuwa a jihar.

Mataimakin sakataren kwamitin birnin Lhasa na jam'iyyar kwaminis ta Sin, kuma shugaban sashin kula da hadin gwiwar jama'a Dawa, wanda ya halarci taron tattaunawar, ya ce, idan aka waiwayi baya a tsawon shekaru 54 da suka gabata, za a gano cewa, da kyar aka kai ga cimma nasarorin da aka samu yanzu, sabo da haka, kamata ya yi a yi farin ciki da abin da ya faru. Ya ce a halin da ake ciki yanzu, musamman yayin da ake sanya wani sabon buri gaba, kamata ya yi a nace ga bin manufa, da inganta hadin gwiwa da ke tsakanin al'ummar yankin, don kokartawa wajen gina birnin Lhasa.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China