in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Siriya ta amince da nadin jami'in kungiyar binciken makamai masu guba da MDD ta yi ga kasar
2013-03-28 15:58:12 cri
A ranar 27 ga wata, kakakin sakatare janar na M.D.D. Martin Nesirky ya bayyana cewa, gwamnatin Siriya ta riga ta amince da nadin jagoran tawagar binciken manyan makamai masu guba na M.D.D. zuwa kasar, a sa'i daya kuma, an ce, yanzu M.D.D. ta shirya tsaf, domin gaggauta gudanar da aiki,

Gwamnatin Siriya ta amince da nadin Ake Sellstrom, kwararre daga kasar Sweden, a matsayin jagoran tawagar binciken ta M.D.D., da sakataren janar na majalisar Ban ki-moon ya yi. Nesirky ya jaddada cewa, dalilin da ya sa za a gudanar da wannan bincike shi ne, don tabbatar da ko akwai makamai masu guba a kasar ko kuwa a'a.

Ban da wannan kuma, an ce, membobin tawagar binciken sun hada da kwararru na hukumar hana yaduwar makaman kare dangi, da na kungiyar kiwon lafiya ta duniya. Haka kuma, Nesirky ya sake jaddada cewa, kamar yadda Ban Ki-moon ya fada, tawagar binciken ta bukaci da a gudanar da aiki cikin 'yanci.

Bisa labarin da aka sanya a kan shafin Internet na M.D.D., an ce, Sellstrom da aka nada a matsayin jagoran tawagar binciken, ya ce, zai fara gudanar da wannan aiki cikin mako mai zuwa.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China