in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya halarci liyafar safe tare da shugabanni da 'yan kasuwa na kasashen BRICS
2013-03-27 16:22:31 cri
Bisa labarin da kamfanin dillancin labarai na XinHua ya bayar, an ce, ran 27 ga watan Maris, a birnin Durban na kasar Afirka ta Kudu, shugaban kasar Sin, Xi Jinping ya halarci taron liyafar safe tare da sauran shugabannin kasashen BRICS da 'yan kasuwa na kasashen. Taron zai sanar da kafuwar kwamitin lura da harkokin kasuwanci da masana'antu na kasashen BRICS.

Yayin taron, masu jagorancin dandalin tattaunawa kan harkokin kasuwanci da masana'antun kasashen BRICS da aka yi a ranar 26 ga wata, za su gabatar wa shugabannin sakamakon tattaunawarsu, da zai hada da shawarwarin da suka shafi ci gaba da hadin gwiwa wajen gina kayayyakin more rayuwa, aikin hakan ma'adinai, aikin noma, sha'anin kudi, makamashi da dai sauransu. Kana shugabannin da suka halarci taron za su ba da jawabi kan sakamakon.

Bisa jadawalin da aka gabatar kafin wannan, za a sanar da labarin kafuwar kwamitin kula da harkokin kasuwanci da masana'antu na kasashen BRICS a yayin taron.(Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China