in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Afrika ta Kudu za su mai da hankali kan inganta tsarin ayyukansu na huldar da kasashe waje
2013-03-26 20:48:27 cri

Kasar Sin da ta Afrika ta Kudu a yau Talata 26 ga wata suka tsai da shawarar mai da hankali a kan dangantakarsu a tsarin huldarsu da kasashen waje, sannan suka yi kira da a samar da wata dama mai wadata da rashin bambanci wajen inganta wannan tsari.

A cikin wata sanarwar hadin gwiwa da suka fitar bayan ganarwasu a birnin Pretoria, shugabannin na Sin Xi Jinping da na Afrika ta Kudu Jacob Zuma gaba dayansu sun amince da cewa, dangantakar hadin gwiwa tana daya daga cikin manyan jigon karfafa zumunci ga ko wace kasa, don haka kasashen biyu suka yi alkawarin inganta wannan fanni zuwa wani sabon matsayi.

A ta fuskar sauran kasashen duniya kuwa, Sin da Afrika ta Kudu sun sha alwashin martaba 'yanci da ra'ayin sauran kasashe masu tasowa sannan kuma za su saka tsari da ka'idoji da ba za su takura ma wadannan kasashen ba a cikin daidaito.

Sai dai kuma shugabannin sun yi kira ga sauran kasashen duniya da su mai da hankali sosai tare da samar da taimakon da ya kamata ma nahiyar Afrika, su mutunta kokarin kasashen Afrika wajen warware matsalolin da suka shafi nahiyar tasu da kansu sannan kuma su taimaka masu wajen inganta kokarin da suke yi ta hanyar samar da ci gaba da kansu.(Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China