in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen BRICS na cikin jerin kasashen da suka fi zuba jari kai tsaye a Afirka
2013-03-26 10:47:00 cri
Ran 25 ga wata, taron cinikayya da neman bunkasuwar MDD ya fidda wani sabon rahoto na nazarin yanayin zuba jarin kasa da kasa, inda ya nuna cewa, bisa nazarin da aka yi game da ajiya da musayar kudi da kasashen ketare suka samar a Afirka, babu shakka, kasashen BRICS sun shiga jerin kasashen da suka fi zuba jari kai tsaye a kasashen Afirka.

Wannan rahoto mai taken 'kasashen BRICS da Afirka' ya nuna cewa, cikin kasashe 20 da suke kan gaba a jerin kasashe da suka fi zuba jari kai tsaye a Afirka, wato idan aka yi nazari kan fannin musayar kudi wajen zuba jari ke nan, za a iya ganin cewa, kasashen Sin, India, da Afirka ta Kudu suna kan matsayin na hudu, biyar da kuma sha bakwai, kana, idan aka juyo kan ajiyar kudi, kasashen Afirka ta Kudu, Sin, India da kuma Rasha suna matsayi na biyar, shida, bakwai da kuma sha biyar.

Rahoton ya kuma bayyana cewa, fannonin da kasashen BRICS suka fi mai da hankula wajen zuba jari a Afirka su ne, sana'o'in kira da hidima, wadanda suka ba da babbar gudumawa wajen samar da karin guraben aikin yi da kuma bunkasa tattalin arziki a kasashen Afirka. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China