in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan tawayen Seleka sun mamaye fadar shugaban kasar Afirka ta Tsakiya
2013-03-24 20:15:24 cri
A ranar Lahadi 24 ga wata, 'yan tawayen Seleka sun yi shelar mamaye fadar shugaban kasar Afirka ta Tsakiya, bayan da a cewarsu shugaban kasar Francois Bozize ya tsere daga fadar.

Wani mai shiga tsakani kan batun kungiyar Seleka ya bayyana wa wakilin kamfanin dillancin labaru na kasar Sin Xinhua cewa, 'yan tawayen Seleka sun riga sun kame fadar shugaban kasar dake birnin Bangui, hedkwatar kasar Afirka ta Tsakiyar.

Ya kara da cewa, "Mulkin shugaba Bozize ya kare a wannan gaba, musamman a wannan lokaci da 'yan tawayen Selekan ke ci gaba da kai hare-hare kan sansanin sojin kasar, da sauran muhimman wurare dake birnin Bangui." A cewarsa ana bukatar mazauna birnin su kasance cikin gidajensu domin samun zarafin maido da daidaito da tsari a birnin.

Wani mazaunin birnin ya bayyana wa 'yan jarida ta wayar tarho cewa, a safiyar Lahadin nan 'yan tawayen Seleka suka rika kai hare-hare, suka kuma kutsa kai cikin birnin Bangui. Kawo yanzu dai, rahotanni na cewa, wasu motocin soja masu tambarin rundunar mayakan Seleka na sintiri a manyan titunan birnin. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China