in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afirka ta Kudu ta yi kokarin tabbatar da tsaron ganawa a tsakanin shugabannin kasashen kungiyar BRICS
2013-03-24 16:24:49 cri

Gwamnatin kasar Afirka ta Kudu ta sanar a ranar 23 ga wata cewa, ta riga ta shirya 'yan sanda 3000 don kara tabbatar da tsaro yayin taron ganawa ta biyar a tsakanin shugabannin kasashen kungiyar BRICS da za a yi a kasar.

Rudunar 'yan sandan kasar Afirka ta Kudu ta bayyana cewa, an riga an tsara wani shirin hadin gwiwa na tabbatar da tsaro yayin da shugabannin kasashen kungiyar BRICS suke ganawa. A halin yanzu, 'yan sanda daga dukkan fadin kasar sun shirya tsaf domin gudanar da aikin tabbatar da tsaro.

Tun daga ranar 26 zuwa ta 27 ga wata ne dai ake sa ran shugabannin kasashen kungiyar ta BRICS za su yi ganawa ta biyar a birnin Durban dake kudu maso gabashin kasar Afirka ta Kudu, inda za su tattauna batun kafa bankin raya kasa, da kara gudanar da ayyukan more rayuwa da dai sauransu. Wannan ne karo na farko da kasar Afirka ta Kudu ta shirya taron kungiyar BRICS tun bayan shigarta kungiyar a watan Disamba na shekarar 2010, kana shi ne karo na farko da aka gudanar da taron a nahiyar Afirka. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China