in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakataren harkokin wajen kasar Amurka ya sake kaiwa yankin Palesdinu da Isra'ila ziyara
2013-03-24 16:19:40 cri
Bayan rikiya da ya yiwa shugaban kasar Amurka Barack Obama a ziyarar da shugaban ya kai yankunan Paledinu da Isra'ila da kuma kasar Jordan, sakataren harkokin wajen kasar ta Amurka John Forbes Kerry ya sake komawa yankin Paledinu da Isra'ila a ranar 23 ga wata don tattauna yadda za a gudanar da shawarwarin shimfida zaman lafiya a tsakanin Palesdinu da Isra'ila tare da hadin kan bangarori daban daban da abin ya shafa.

A ranar 23 ga wata, Kerry ya gana da shugaban hukumar al'ummar Palesdinu Mahmoud Abbas a Amman, babban birnin kasar Jordan, inda daga bisani ya koma kasar Isra'ila. A wannan rana da dare, ya yi shawarwari tare da firaministan kasar Isra'ila Benjamin Netanyahu, inda suka tattauna kan yadda za a sake bude shawarwarin shimfida zaman lafia a tsakanin Isra'ila da Palesdinu. Yanzu shekaru biyu ko fiye ke nan da aka dakatar da shawarwarin tsakanin Isra'ila da Palesdinu. Ba a cimma tudun fadawa a yayin da Obama yake kan kujerar shugaban kasar karo na farko ba. A yayin da shugaban kasar Amurka Obama yake ziyara a yankin Palesdinu da Isra'ila, ya yi alkawari cewa, Kerry zai yi kokarin taimakawa wajen warware matsaloli a tsakanin Palesdinu da Isra'ila, amma shugaba Obama bai gabatar da sabon shirin warware wannan batu ta hanyar diplomasiyya ba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China