in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Sin ya gana da manzon musamman na shugaban kasar Amurka
2013-03-20 20:33:54 cri
A ranar Laraba 20 ga wata a nan birnin Beijing, firaministan kasar Sin Li Keqiang, ya gana da manzon musamman na shugaban kasar Amurka, kuma ministan kudi na kasar, Jacob Lew, inda Li ya furta cewa, kamata ya yi kasashen biyu su kara amincewa da juna, da kara samun moriyar juna, a kokarin kafa sabuwar dangantaka tsakanin manyan kasashen biyu.

Li ya bayyana cewa, yanzu dangantaka tsakanin Sin da Amurka na kasacewa cikin muhimmin mataki, don haka kamata ya yi a sa kaimi ga bunkasa dangantakar abokantaka da hadin gwiwa, mai cike da girmama juna, bisa matsaya daya da shugabannin kasashen biyu suka cimma.

A cewar firaminista Li, gwamnatin kasar Sin za ta ci gaba da dora muhimmanci kan dangantaka tsakaninta da Amurka, da fatan za a sa kaimi ga raya dangantakar zuwa mataki na gaba, a fannonin hadin gwiwa da juriya, da kuma yin takara mai kyau tsakanin su, a kokarin samar da yanayi mai nagarta.

A nasa bangare, Jacob Lew ya bayyana cewa, Amurka na fatan sa kaimi ga hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu, bisa yin shawarwari a fannin tattalin arziki da manyan tsare-tsare tsakanin kasashen biyu, da fatan kasahsen 2 za su kara mu'amala da juna, wajen tsara ka'idojin kasashen duniya, tare da karfafa hadin gwiwa kan tinkarar sauyawar yanayi da sauransu.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China