in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude bikin "fahimtar Sin" a Brassaville na jamhuriyar kasar Congo
2013-03-20 14:48:14 cri
Ran 19 ga watan Maris, shekarar 2013, aka bude bikin "fahimtar Sin a kasar Congo(Brassaville)" a birnin Brassaville, bisa kiran gamayya da ofishin labaran majalisar gudanarwar kasar Sin, ofishin jakadancin Sin da ke jamhuriyar kasar Congo, ma'aikatar lura da harkokin waje da na hadin gwiwar jamhuriyar kasar Congo, ma'aikatar harkokin al'adu da fasahohi, ma'aikatar ba da ilimin kwalejoji, ma'aikatar kula da harkokin labarai da dangantakar majalisar dokokin kasar.

Shugaban jamhuriyar kasar Congo Denis Sassou-Nguesso, mataimakin darektan ofishin yada labaran majalisar gudanarwar Sin Wang Guoqing, jakadan Sin da ke kasar Congo Guan Jian, wasu ministocin kasar Congo, har ma da wasu jakadun wassu kasashen dake kasar Congo sun halarci bikin bude aikin da aka yi a cikin harabar majalisar dokokin kasar Congo.

A jawabinsa wajen bikin, mataimakin darektan ofishin yada labaran majalisar gudanarwar Sin Wang Guoqing ya bayyana cewa, an fara aikin "fahimtar Sin" a jamhuriyar kasar Congo kafin sabon shugaban kasar Sin Xi Jinping zai kai ziyarar aiki a kasar. Ana sa ran cewa, al'ummomin kasar Congo za su samu cikakken fahimta game da kasar Sin bisa fannoni daban daban ta aikace-aikacen da dama da za a shirya, misali, wasan kwaikwayo, nune-nunen bidiyo, intabiyun kafofin watsa labarai, kafuwar dakin nunin harkokin Sin da dai sauransu.

Ministan ma'aikatar kula da harkokin labarai da dangantakar majalisar dokokin kasar Congo(Brasseville) ya bayyana a wajen bikin cewa, al'adun kasar Sin na da dogon tarihi, kuma ya zuwa shekarar 2014, za a cika shekaru 50 da aka kulla dangantakar diflomasiya tsakanin kasashen Sin da kasarsa, don haka, ziyarar da shugaban kasar Sin zai yi a kasar Congo(Brasseville) za ta karfafa zumuncin tsakanin kasashen biyu, da kuma inganta cudanyar al'adun tsakaninsu.

Ban da wannan kuma, a daren wannan rana, 'yan wasan fasahar tawagar wasan kundunbala ta kasar Sin sun nuna wasannin gargajiyar Sin da suka hada da wake-wake da raye-raye, wasan dabo, da kuma wasan kundunbala, wadanda suka kayatar da baki sosai a wurin. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China