in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mauritius za ta karbi bakuncin taron UNESCO kan sauyin yanayi
2013-03-20 14:09:28 cri

Taron shiyya na kwararrrun hukumar kula da ayyukan ba da ilmi da kimiyya da kuma al'adu UNESCO na fadakarwa kan sauyin yanayi domin samun cigaba mai karko da karbuwa a Afrika zai gudana a Mauritius a yau ranar Laraba. Dandalin na kwanaki uku zai tattara kimanin wakilai dari daga yankunan gabashin Afrika, kuriyar Afrika da tekun Indiya, kuma zaman taron zai mai da hankali kan kalubale da sauyin yanayi ke iyar kawowa ga tsare-tsaren ilimantarwa a Afrika da matsayin da ilmi zai kawo ga karbuwa da rage kaifin sauyin yanayi. Mahalarta taron za su bullo da tsarin aiki na bunkasa ba da ilmi a matsayin wani muhimmin makami wajen kyautata karbuwar sauye-sauyen yanayi bisa manufar samun cigaba mai karko a kasashen Afrika. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China