in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bankin duniya zai ba da taimakon kudi na dallar Amurka miliyan 150 ga kasar Mali
2013-03-19 16:12:39 cri
Ran 18 ga wata, mataimakin shugaban kula da harkokin yankin Afirka na bankin duniya Abdoulaye Makhtar Diop ya bayyana a babban birnin kasar Mali, Bamako cewa, bankin duniya zai ba da taimakon kudi na dallar Amurka miliyan 150 ga kasar Mali, don bunkasa ayyukan noma da ba da tabbaci ga zaman al'umma.

Mr. Abdoulaye Makhtar Diop ya kuma jadadda cewa, sabo da a halin yanzu, karancin abinci, tabarbarewar yanayin tsaro, da kuma rikicin siyasa da kasar Mali ke fama da su, sun riga sun kawo illa ga bunkasuwar tattalin arzikin kasar, dalilin haka, kasar take bukatun taimakon gamayyar kasa da kasa sosai. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China