in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya yi kiran hadin gwiwar bunkasa kawance tsakanin Sin da Amurka
2013-03-19 15:36:59 cri

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana yau Talata cewa, kasar Sin a shirye take ta hada hannu da kasar Amurka a fuskar bunkasa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu.

Xi ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da sakataren baitulmalin Amurka Jacob Lew, wanda zai kawo ziyara nan birnin Beijing ranar Talata da Laraba.

Shugaban ya yaba kyakyawan sakamako da dangantaka dake tsakanin kasashen biyu ta haifar, cikin shekaru talatin da suka gabata, inda jama'ar kasashen biyu suka amfana tare kuma da bunkasa zaman lafiya da daidaito a yankin Asiya-pasifik da ma duniya baki daya.

Lew ya taya Xi murna dangane da hayewa mukamin shugaban kasar Sin.

Ya yi kira ga bangarorin biyu da su bunkasa dangantaka a fannin tattalin arziki da muhimman batutuwa da kasashen biyu suke fuskanta da kuma tafi da banbanci dake tsakaninsu yadda ya kamata.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China