in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kammala zaben raba gardama a Zimbabwe cikin kyakkyawan yanayi, in ji kungiyar SADC
2013-03-18 09:40:52 cri

Tawagar sa ido kan zaben raba gardama da aka gudanar a kasar Zimbabwe, ta kungiyar kasashen kudancin Afirka SADC, ta amince da yadda wannan zabe ya gudana cikin managarcin yanayi. Jagoran tawagar kuma ministan harkokin wajen kasar Tanzania Bernard Membe ne ya bayyana hakan ga manema labaru, yana mai cewa, an gudanar da zaben lami lafiya, ba kuma tare da wani korafi na magudi ba.

A ranar Asabar din da ta gabata ne dai al'ummar kasar ta Zimbabwe suka kada kuri'unsu, kan batun amincewa da daftarin kundin dokokin kasar, wanda tuni ake hasashen zai samu amincewa da gagarumin rinjaye, ganin yadda manyan jam'iyyun kasar suka nuna goyon bayansu gare shi, kafin kada kuri'un al'ummar kasar.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China