in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan bindiga sun saki 'yan fursuna yayin hari a gidan yari a Najeriya
2013-03-16 16:35:13 cri
Wata kafar 'yan sanda ta bayyana wa kamfanin dllancin labaran kasar Sin, Xinhua cewa, wasu 'yan bindiga da ake kyautata zaton 'yan kungiyar Boko haram ne sun kai hari a wani gidan yari dake yankin arewa maso gabashin Najeriya, inda suka kashe wani dan unguwar suka kuma saki 'yan fursuna da dama.

'Yan sandan sun tabbatar da harin bayan da mazauna jihar Borno suka kai rahoto cewa 'yan bindiga sun kai farmaki a gidan yari da misalin karfe 7 na daren lokacin wurin, ranar Alhamis.

Ana kyautata zaton cewa wadanda suka kai harin su ne wadanda suka kai farmaki a tashar 'yan sanda dake Gwoza a kan iyakar kasar Najeriya da Kamaru kwanaki 10 da suka wuce inda suka kashe mutane 8 har da dan sanda daya.

Kafar ta tsaro ta ce 'yan kungiyar Boko Haram din sun kai farmaki a gidan yarin ne saboda akwai wasu daga cikin mamabobinsu da aka cafke yayin hare hare na baya da ma kan wasu laifuka wadanda suke kulle a gidan yarin Gwoza.

Gwoza karamin gari ne dake da nisan kilomita 134 a kudu maso gabashin garin Maiduguri inda a nan ne ake fama da 'yan kungiyar Boko Haram, kuma a lokuta da dama gwamnatin Najeriya ta sha kafawa da kuma daga dokar ta baci a yankin saboda hare hare. (Lami Ali)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China