in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Sudan,.Masar da Libya sun cimma yarjejeniyar hako ma'adinai
2013-03-15 11:02:44 cri

A ranar Alhamis ne kasashen Sudan, Masar da Libya suka cimma yarjejeniyar karfafa hadin gwiwa a bangaren albarkatun ma'adinai don biyan bukatun tattalin arzikin kasashen uku.

A ranar ta Alhamis ce aka fara tattauna tsakanin kasashen uku a birnin Khartoum a bangaren hako ma'adinai, ganawar da ta samu halartar ministan ma'adinan kasar Sudan Kamal Abdullatif, ministan man fetur da albarkatun ma'adinai na kasar Masar Osama Kamal da kuma ministan masana'antu na kasar Libya Suleiman Ali Al-Fitory.

Taron ya tattauna batun kafa asusun hako ma'adinai na hadin gwiwa don daukar nauyin ayyukan hako ma'adinai a kasashen na Larabawa ta hannnun kawancen kasashen Larabawa tare da gudanar da nazari don gano hanyoyin da suka dace na hako albarkatun ma'adinai.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China