in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi suka dangane da harin da ake kaiwa a Kwadibwa
2013-03-15 09:38:41 cri

A ranar Alhamis din nan ne mai magana da yawun MDD Eduardo del Buey ya bayyana cewa, hukumar MDD dake aiki a kasar Kwadibwa ta yi tir da mummunan harin da aka kai ranar Laraba a wani kauye dake yammacin kasar ta yammacin Afirka, kana an yi kira ga ma'aikatan kiyaye zaman lafiya na MDD a yankin da su kasance cikin shiri.

Yayin jawabi da aka saba yi kowace rana ga manema labaru Edwardo del Buey ya ce, ofishin MDD a Kwadibwa ya yi tir da kisan mutane hudu a wani harin da wasu wadanda ba'a san ko su waye ba suka kai ranar Laraba, a kauyen Zilebly a yankin yammacin kasar.

Ya ci gaba da cewa, an bukaci ma'aikatan kiyaye zaman lafiya na MDD a kasar da su kasance cikin shirin ko ta kwana, su kuma kasance cikin shirin don tallafawa dakarun Kwadibwa.

Ya kara da cewa, MDD a shirye take ta taimaka wa gwamnatin Kwadibwa a yunkurinta na tabbatar da kafuwar dawowar zaman lafiya a kasar.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China