An kira cikakken zama na hudu na babban taron farkon wakilan jama'ar kasar Sin karo na sha biyu a babban dakin taron jama'a ran 14 ga wata da safe, inda ta hanyar kada kuri'un da ba su nuna sunaye ba, an zabi Mr. Xi Jinping a matsayin shugaban jamhuriyar jama'ar kasar Sin, da kuma shugaban kwamitin tsakiyar na harkokin sojan kasar Sin, kuma an zabi Mr. Zhang Dejiang a matsayin shugaban zaunannen kwamitin babban taron wakilan jama'ar Sin karo na sha biyu, yayin da Mr. Li Yuanchao a matsayin mataimakin shugaban jamhuriyar jama'ar kasar Sin. Bugu da kari, an zartas da kudurin gyare-gyaren tsarin majalisar gudanarwa da canje-canjen ayyukanta yayin wannan taro.