in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta yi maraba da ra'ayin kasar Amurka game da bunkasuwar kasar Sin
2013-03-12 20:17:21 cri
Game da jawabin mai ba da taimako ga shugaban kasar Amurka ta fuskar tsaro Thomas Donilon, inda ya bayyana cewa, kasar Amurka ta yi maraba da bunkasuwar kasar Sin cikin lumana, kakakin ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin Hua Chunying ta bayyana a ranar 12 ga wata a nan birnin Beijing cewa, kasar Sin ta yi maraba da irin wannan ra'ayin da Donilon ya bayar, kana Sin tana son kara yin hadin gwiwa a tsakaninta da kasar Amurka wajen inganta sabuwar dangantakarsu.

A jiya Talata 11 ga wata, Thomas Donilon ya yi jawabi mai lakabin "Manufar kasar Amurka game da yankunan Asiya da tekun Fasific", inda ya bayyana manufar kasar Amurka da za a aiwatar ga kasar Sin a yayin wa'adi na biyu na mulkin shugaban kasar Barack Obama. Ya bayyana cewa, kasar Amurka ta yi maraba da bunkasuwar kasar Sin cikin lumana, kuma za ta ci gaba da dora muhimmanci kan dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, da kara yin mu'amala da hadin gwiwa tare da Sin, da warware matsalolinsu yadda ya kamata, da kuma yin kokari tare wajen inganta sabuwar dangantakarsu da dai sauransu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China