in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana sa ran sake ma'aikatan kiyaye zaman lafiya na MDD da aka tsere a ranar 9 ga wata
2013-03-09 16:54:36 cri
Sashin kula da ayyukan kiyaye zaman lafiya na MDD ya fayyace a jiya Jumma'a ranar 8 ga wata cewa, ma'aikatan kiyaye zaman lafiya guda 21 na rundunar masu aikin sa ido ta MDD da 'yan adawa na kasar Sham suka tsare a tudun Golan suna lafiya, kuma ana sa ran sake su a ranar 9 ga wata.

Kakakin sashen ya yi bayani a wannan rana cewa, bangarorin da abin ya shafa sun riga sun shirya sosai kan sake dukkan ma'aikatan kiyaye zaman lafiya guda 21 da aka tsare. Rundunar masu aikin sa ido ta riga ta aika da ma'aikatanta zuwa kauyen Jemra da wadancan ma'aikata 21 suke a daren ranar, to amma saboda yin la'akari da tsaro ne, za a gudanar da aiki a ranar 9 ga wata.

Kafin wannan, kwamitin sulhu na MDD ya yi shawarwari cikin sirri a wannan rana, inda aka saurari rahoton da mataimakin sakataren MDD dake kula da harkokin kiyaye zaman lafiya, kuma daraktan sashen kiyaye zaman lafiya, Herve Ladsous ya bayar game da sabon yanayin da ake ciki, inda ya ce, wadannan ma'aikata guda 21 suna dakunan dake karkashin wasu gidaje na kauyen Jemra inda aka tsare su, kuma suna cikin koshin lafiya.

Jami'an MDD suna kokarin neman ganin an sake su da wuri. Kasashen MDD sun bayyana baki daya cewa, za su ci gaba da nuna goyon baya ga kokarin da MDD ke yi na sake ma'aikatan. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China