A kwanan nan ne, fadar shugaban kasar Afrika ta Kudu ta yi kokarin kawar da wani fargaba dake da nasaba da lafiyar shugaban kasar Jacob Zuma.
Sakamakon binciken lafiyar Zuma, ya kasance mai gamsarwa bayan an gudanar da binciken koshin lafiya na shekara shekara, in ji kakakin fadar shugaban kasar, Marc Maharaj.
Mista Marahaj ya yi wannan sanarwa ne bayan da aka gudanar da binciken lafiyar shugaba Zuma na shekara shekara a ranar Labara a wasu asibitoci uku dake birnin Durban. (Maman Ada)