Manufofin kudi da Sin za ta aiwatar da su a bana za su taimaka wajen raya tattalin arziki da kuma kiyaye farashin kaya a kasar
Memban majalisar bada shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin kuma shugaban bankin jama'ar kasar Sin Zhou Xiaochuan ya bayyana a ranar 6 ga wata cewa, manufofin kudi da kasar Sin za ta aiwatar da su a bana na dacewa da halin kasar take ciki. Yanzu an fi daukar matakan tsuke bakin aljihu idan aka kwatanta da lokacin tinkarar rikicin hada-hadar kudi na duniya, wadanda kuma suka taimaka wajen cimma burin bunkasuwar tattalin arziki da kiyaye farashin kaya a kasar Sin da aka tanade a rahoton gwamnatin kasar. (Zainab)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku