in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata Japan ta yi hadin gwiwa da Sin wajen warware batun tsibirin Diaoyu
2013-03-05 16:16:52 cri
A yau Talata 5 ga wata ne mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin Zhang Zhijun, ya bayyana wa manema labarai cewa, kamata ya yi kasar Japan ta yi hadin gwiwa tare da kasar Sin, wajen warware matsalar tsibirin Diaoyu. Ya kuma jadadda cewa, Sin na fatan za a kai ga warware matsalar yadda ya kamata, amma ba za ta yarda da daukar matakan tozarta ikonta kan tsibirin ba.

Mr. Zhang Zhijun, ya bayyana hakan ne gabanin shigarsa babban dakin taron jama'ar kasa da ke birnin Beijng, inda aka bude taron farko na sabuwar majalisar wakilan jama'ar kasar Sin karo na 12 a yau Talata 5 ga wata. Zhang Zhijun ya kuma jadadda cewa, kasar Sin ba za ta canja matsayinta kan batun tsibirin na Diaoyu ba.

Haka zalika, ya kuma nuna cewa, kasar Sin za ta karfafa ayyukanta da suka shafi teku, ciki hadda bunkasa tattalin arzikin teku, da kiyaye muhallin teku, da kiyaye ikon kasar kan teku yadda ya kamata, baya ga ci gaba da kare dokokin teku. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China