in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gudanar da taron manema labaru na cikakken zaman taron farko na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin karo na 12
2013-03-04 16:11:34 cri

A Litinin din nan ranar 4 ga wata wajen karfe 11 na safe ne, a babban dakin taruwar jama'a, aka gudanar da taron manema labaru na cikakken zaman taron farko na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin karo na 12, kuma sabuwar kakakin taron Fu Ying ta gabatar da ajandar taron da aikin majalisar wakilan jama'a, kuma ta zanta da manema labaru na gida da waje game da tsarin majalisar wakilan jama'a, da manufar diplomasiyyar kasar, da batun yaki da cin hanci da rashawa, da sa ido game da basussukan da kananan hukumomin kasar suka ci.

Yayin da Fu Ying ke zantawa da manema labarun, ta bayyana cewa, game da tsokanar da wasu kasashe suke yi, don gane da rikicin yankunan kasar, kamata ya yi Sin ta daidaita tare da magance rikicin cikin hanzari.

Da take amsa tambayar ko kasar Sin za ta dauki kwararan matakai don daidaita batutuwa da kasashen waje, Fu Ying ta bayyana cewa, kasar Sin ta sha bamban da manyan kasashen duniya, kuma tana da tsarin siyasa na daban, tare da tarin yawan al'umma, da samun saurin karuwar tattalin arziki, kuma har yanzu, tana ci gaba da saurin bunkasuwa, sabo da haka, wanda hakan ne ya sa wasu mutane ba sa fahimta kasar Sin sosai, haka kuma, akwai wasu mutane dake ci gaba da hasashen makomar kasar Sin bisa dangantakar kasa da kasa cikin shekaru 500 da suka gabata, wato idan kasar ta samu karfi, tabbas ne za ta ci gaba da daukar tsattsauran matakai, haka kuma, masu irin wannan tunani na gaggauta lalubo shaidun tabbatar da wannan zato nasu.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China