in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Masar ya gana da sakataren harkokin wajen kasar Amurka
2013-03-04 15:44:57 cri
A ranar 3 ga wata, bisa labarun da kamfanin dillancin labaru na kasar Masar ya bayar, an ce, a wannan rana, shugaban kasar Masar Mohamed Morsy ya gana da sabon sakataren harkokin wajen kasar Amurka John Kerry wanda ke yin ziyara a kasar.

Haka kuma, bangarorin biyu sun tattauna batutuwan yunkurin siyasa a kasar Masar, da halin da ake ciki a kasar Siriya, da maganar samar da zaman lafiya a yankin Gabas ta tsakiya da sauransu. Kazalika kuma, Kerry ya yaba wa Shugaba Morsy kan kokarin da ya yi na daidaita rikicin da ke tsakanin Isra'ila da kungiyar Hamas cikin nasara, kuma ya ce, Amurka tana ganin cewa, ba za a iya rasa taimakon kasar Masar ba cikin yunkurin samar da zaman lafiya a yankin Gabas ta tsakiya, ban da wannan kuma, bangarorin biyu sun tattauna matakan da Amurka za ta dauka wajen taimakawa Masar farfado da tattalin arziki, cikinsu har da ba da kudin agaji da kara fadada yawan kayayyakin da kasar take fitarwa.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China