in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manema labaru na gida da wajen kasar Sin fiye da dubu 3 za su tattara labaru a kan tarurrukan NPC da CPPCC
2013-03-02 17:04:52 cri

Za a bude zaman taro na farko na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin NPC karo na 12 a ranar 5 ga wata, yayin da za a a bude zaman taro na farko na majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin CPPCC karo na 12 a ranar 3 ga wata. An labarta cewa, ya zuwa karfe 12 na ranar Jumma'a 1 ga watan Maris, yawan manema labaru na gida da wajen kasar Sin da za su tattara labaru kan tarurrukan NPC da CPPCC ya wuce dubu 3, ciki har da wadanda suka fito daga kasashen waje kusan dubu 1, sa'an nan na yankunan Hong Kong , Macao da Taiwan sun zarce dari 4.

Wadannan manema labaru da suka fito daga kasashen ketare wasunsu suna aiki a wasu muhimman kafofin yada labaru na kasashe masu sukuni, wasu kuma sun fito daga kafofin yada labaru na kasashen Afirka da Latin Amurka da sauran kasashe masu tasowa. Batutuwan da suke jawo hankalinsu su ne manufofin tattalin arzikin kasar Sin, yanayin tattalin arzikin kasar Sin a nan gaba, yiwuwar da ke akwai ga kasar Sin na aiwatar da sabuwar manufar sa kaimi kan bunkasar tattalin arziki, matakan da Sin za ta dauka wajen taimakawa warware rikicin basusukan Turai da dai sauransu. Ban da wannan kuma, kafofin yada labaru na kasashen ketare sun fi mai da hankali kan yadda kasar Sin za ta kyautata zaman rayuwar fararen hula, kamar ba da tabbacin zaman rayuwa, yin kwaskwarima kan aikin jinya da tsarin ba da ilmi da kuma daidaita farashin gidaje a kasuwar kadarori da dai sauransu.(Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China