in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijeriya ta aike da sojojin kasa na karshe zuwa kasar Mali
2013-03-01 11:01:31 cri
Ran 27 ga watan Fabrairu, Nijeriya ta kammala ayyukan aikewa da sojojin kasa zuwa kasar Mali bisa kiran kungiyar magoya bayan kasar Mali ta kasa da kasa da ke karkashin jagorancin kasashen Afirka, don fatattakar dakaru masu tsattauran ra'ayin Islama dake yankin arewacin kasar Mali.

Ma'aikatar kula da harkokin tsaron kasar ta Nijeriya ta bayyana cewa, ya zuwa yanzu dai, gwamnatin kasar ta cika alkawarinta na aikewa da sojojin kasa guda 1200 zuwa kasar Mali, bayan wadannan sojojin na karshe guda 162 sun isa kasar.

A ran 27 ga watan da ya gabata, yayin taron manema labarai da aka kira a birnin Abuja, kakakin kwamitin kula da labaran tsaron kasar Nijeriya ya nuna cewa, cikin wata guda da ya gabata, sakamakon fuskantar yanayin tabarbarewar tsaro a kasar, da kungiyoyi masu tsattsauran ra'ayi, musamman ma kungiyar Boko Haram suka haddasa, rundunar sojan kasar Nijeriya ta horas da sojojin musamman fiye da dubu 2, wajen yaki da su, amma a halin yanzu, Nijeriya ta riga ta aika da galibin sojojin zuwa wurare mafi fama da rikici a kasar Mali.

Bugu da kari, bayan kasar Faransa ta janye sojojinta guda dubu 4 daga kasar Mali a watan Maris, sojojin Nijeriya da ma sauran sojoji da kasashen Afirka suka tura wa kasar Mali za su kara taimaka cikin yakin, da kuma kiyaye zaman lafiya a kasar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China