in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta yi kira ga masana'antun kasa da suka zuba jari a kasashen waje da su kiyaye muhalli
2013-02-28 16:05:54 cri
Bisa labarin da wakilinmu ya samu daga ma'aikatar kula da harkokin kasuwanci ta Sin, an ce, kwanan baya, ma'aikatar kula da harkokin kasuwanci da ma'aikatar kiyaye muhalli sun ba da wata takardar kiyaye muhalli game da masana'antun Sin da suka saka jari a kasashen waje, don jagorancin masana'antun da su kara kiyaye muhalli yayin da suke zuba jari a kasashen waje.

Takardar kiyaye muhalli ta yi kira ga masa'antu da su kara mai da hankali game da kiyaye muhalli, da daukar alhakin da ke wuyansu wajen kiyaye muhalli, don cimma moriyar arziki da kiyaye muhalli tare, haka kuma, an yi kira ga masana'antu da suka je saka jari a kasashen waje da su bi dokokin wurin, kazalika ma, an bukaci ayyukan yin hadin kai wajen saka jari dake gudana a kasashen waje da suka samu izni daga hukumomin kula da harkokin kiyaye muhalli na wurin, su sauke nauyin da ke bisa wuyansu ta fannin kiyaye muhalli kamar yadda doka take bukata, haka kuma, an sa kaimi ga masana'antun da su yi nazari da koyi da ka'idoji da dokoki dake shafar kiyaye muhalli na kungiyoyin kasa da kasa da hukumomin hada-hadar kudi na kasashensu.

Ya zuwa karshen shekarar 2011, yawan masana'antun da Sin ta kafa a kasashen waje ya kai dubu 18, wadanda suke kasashe da yankuna 177, kuma yawan jarin da Sin ta saka kai tsaye ya kai kudin Amurka wato dalar biliyan 424.78. (Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China