in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wani babban jami'in tsaro ya tsallake rijiya da baya a kasar Libya
2013-02-28 09:43:17 cri

Rahotanni daga kasar Libya sun bayyana aukuwar wani yunkuri na kisan Jala Al-Regi, wanda ke matsayin kwamandan bataliyar babban kwamitin tsaron kasar, da yammacin ranar Laraba 27 ga watan nan.

Harin wanda ake zaton na ramuwar gayya ne, ya faru ne a yankin Tajoora, yanki mafi girma dake wajen babban birnin kasar wato Tripoli. Maharin dai ya tsere bayan yunkurin kisan Al-Regi, ko da yake dai hakarsa bai cimma ruwa ba.

Bisa labarin da aka samu, an ce, kafar Al-Regi ta samu rauni sakamakon harbin bindiga har guda 5, inda a yanzu haka yake asibiti domin samun kulawar likitoci. Tuni kuma jami'an tsaro suka fara gudanar da bincike kan aukuwar wannan lamari.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China