in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a samu kyakkyawar makoma kan bunkasuwar dangantakar dake tsakanin Sin da kasashen Afirka
2013-02-27 20:25:17 cri
Shugaban sashen kula da harkokin Afirka na ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin Lu Shaye ya bayyana a ranar 27 ga wata cewa, akwai albarkatu da kuma kasuwanni masu yawa a kasashen Afirka, don haka za a samu kyakkyawar makoma kan bunkasuwar dangantakar dake tsakaninsu da kasar Sin.

Lu Shaye ya bayyana a gun taron tattaunawa kan harkokin diplomasiyya da aka yi a kan shafin internet a wannan rana cewa, yana fatan bangarori daban daban za su kara sa lura kan nahiyar Afirka, da kuma inganta dangantakar dake tsakanin Sin da kasashen Afirka zuwa wani sabon matsayi.

Lu Shaye ya nuna cewa, a sabon karnin da ake ciki, an samu babban ci gaba kan hadin gwiwa a tsakanin Sin da kasashen Afirka, yawan kudin ciniki a tsakaninsu da aka samu a kowace shekara ya kai kimanin dala biliyan 200, kana yawan jarin da kasar Sin ta zuba a kasashen Afirka ya kai dala biliyan 17. Ban da wannan kuma, an kara yin mu'amala a tsakanin jama'ar bangarorin biyu. Yawan Sinawa da suke zuwa kasar Afirka ta kudu a kowace shekara ya kai dubu 100, kana yawansu da suka je kasar Seychelles ya kai dubu 4, adadin da ya ninka cikin sauri. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China