in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An samu mataki na farko kan yadda za a kaddamar da hakikanin shawarwari kan batun nukiliya na Iran
2013-02-27 20:10:02 cri
A ranar Laraba 27 ga wata, Hua Chunyin, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta bayyana a nan Beijing cewa, an samu ci gaba a gun shawarwarin da aka yi kan batun nukiliya na Iran da aka yi a Alma-atu na kasar Kazakstan, hakan ya sa aka shiga mataki na farko kan yadda za a kaddamar da hakikanin shawarwari kan batun nukiliya na Iran. Sabo da haka, kasar Sin na fatan bangarorin da abin ya shafa za su nuna sahihanci da daukar matakai na zahiri, ta yadda za a iya kara ciyar da shawarwarin gaba cikin hanzari.

Madam Hua ta nuna cewa, kasar Sin na tsayawa tsayin daka kan matsayinta na neman sulhu a tsakanin bangarori daban daban. A shekarar ta 2006 ne aka shigar da kasar Sin cikin tsarin kasashe 6, sannan ta tura wakilanta zuwa shawarwarin da aka yi tsakanin wadannan kasashe 6 har sau 4, da wani taron kwararru kan batun. Haka kuma, a cikin wadannan shekaru da yawa da suka gabata, bangaren Sin ya yi kokarin yin mu'amala tsakaninsa da sauran bangarori daban daban, kuma ya yi kokarin neman sauran bangarori da su dauki matakai bisa hakikanin halin da ake ciki, ta yadda za a iya kulawa da abubuwa daban daban na bangarori daban daban domin lalubo shirin da ya dace, har ma kasar Sin ta fitar da shawara mai amfani domin kokarin kawar da sabane-sabanen da ke kasancewa a tsakanin bangarori daban daban da neman matsaya daya. Sakamakon haka, bangarori daban daban suka yaba wa kyakkyawar rawar da kasar Sin ke takawa kan batu. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China