in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar EU tana fatan Iran za ta nuna sassauci game da batun nukiliyarta
2013-02-27 16:00:30 cri

A ranar 26 ga wata, a birnin Almaty da ke kasar Kazakhstan, kakakin babban wakili game da manufofin diplomasiyya da tsaro na kungiyar EU Michael Mann, ya bayyana cewa, kungiyar EU tana fatan Iran za ta nuna sassauci game da shawarwari kan batun nukiliyarta, duk da rashin tabbas don gane da yanke wata shawara a yayin wannan taro.

Michael Mann ya ce, kungiyar EU ta riga ta gabatar da sabon shirin shawarwari, kuma tana fatan Iran za ta nuna saukin kai, tare da yin rangwame game da wasu batutuwa.

Ya ce, mai yiwuwa ne, kasashe 6 da batun nukiliyar kasarta Iran ya shafa, wato Amurka, da Birtaniya, da Faransa, da Rasha, da Sin da kuma Jamus, za su yi shawarwari da kasar Iran, game da fasahohin nukiliya, ko da yake dai hakan ya danganta ga matsayin kasar ta Iran, da ci gaba da za a samu game da batun nukiliyar kasar.

A wannan rana, an yi shawarwari tsakanin kasar Iran da kasashe 6 da batun nukiliyar Iran ya shafa da kuma kungiyar EU a birnin Almaty, wato birni mafi girma a kasar Kazakhstan, kuma wannan shi ne karo na farko da aka koma teburin tattaunawa game da batun nukiliya na kasar ta Iran, tun bayan watanni 8 da dakatar da hakan.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China