in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Somaliya ta farfado da huldar diflomasiyya tsakaninta da wasu kasashen Turai biyar
2013-02-27 10:33:30 cri
Ran 26 ga wata, shugaban kasar Somaliya Hassan Sheikh Mohamud, ya karbi takardun kama aiki daga sabbin jakadun kasashen Jamus, da Faransa, da Spaniya, da Belgium da kuma Finland, wadanda suka gabatar a fadar gwamnatin kasar dake birnin Mogadishu. Wannan mataki dai ya nuna cewa, kasar ta Somaliya ta farfado da huldar diflomasiyya tsakaninta da wadannan kasashen biyar ke nan a hukumance.

Bayan karbar takardun aikin, shugaba Hassan Sheikh Mohamud, ya yi shawarwari tare da jakadun biyar, inda ya bayyana cewa, lamarin farfado da dangantakar diflomasiyya tsakanin kasarsa da kasashen Turan 5, ya nuna a fili, irin amincewar da gamayyar kasa da kasa ke yi, ga yunkurin gwamnatinsa ta fuskar samar da ci gaba, shugaban ya kuma ba da tabbacin ba da dukkanin gudumawa ga harkokin ci gaban duniya.

A jawabinsa jakadan kasar Faransa a Somaliya cewa ya yi, lamarin farfadowar huldar difliomasiyya wani babban ci gaba ne da aka samu, don gane da dangantakar kasashen biyu, domin kuwa cikin shekaru 20 da suka gabata, kasar ta Faransa ba ta taba aikewa da jakada zuwa kasar Somali ba, amma a halin yanzu, kasashen biyu za su farfado da dangantakar aminci tsakaninsu, kan fannonin daban daban da suka hada da siyasa, da tsaro, da ci gaba da dai sauransu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China