in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashe shida da batun nukiliya na kasar Iran ya shafa suna fatan za a samu ci gaba a shawarwarin da ake yi a Alma-ata
2013-02-26 20:10:29 cri
Michael Mann, kakakin babbar wakiliyar kungiyar EU mai kula da harkokin diplomasiyya da manufofin tsaro Catherine Ashton ya bayyana a ranar 26 ga wata cewa, kasashe shida da batun nukiliya na kasar Iran ya shafa wato Amurka, Ingila, Faransa, Jamus, Rasha da kuma Sin sun yi fatan za a samu ci gaba a shawarwarin da ake yi a Alma-ata dake kasar Kazakhstan.

Mr Mann ya bayyana hakan ne a gun taron manema labaru da aka gudanar a yayin da ake yin shawarwari kan batun nukiliya na kasar Iran a Alma-ata.

Hakazalika Mann ya nuna cewa, akwai sauran tafiya wajen warware batun nukiliya na kasar Iran. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China