in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a cimma nasarar shawarwari kan batun nukiliya idan kasashe 6 suka amince da ikon Iran kan mallakarsa
2013-02-20 15:00:11 cri
A ranar 26 ga wata, kasar Iran da kasashe shida da ke kula da batun nukiliyar kasar, za su yi shawarwari a birnin Alma-Ata da ke kasar Kazakhstan.

Don gane da hakan, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Iran Mechman Palasite ya bayyana cewa, za a samu sakamako mai gamsarwa cikin shawarwarin da za a yi a makon mai zuwa, muddin dai kasashe shida watau kasashen Amurka, Burtaniya, Faransa, Rasha, Sin da Jamus su amince da ikon kasar Iran kan mallakar nukiliyar.

Yayin taron manema labarai da ma'aikatar harkokin wajen kasar ta kira a

ranar 19 ga watan nan, Mechman Palasite ya bayyana cewa, kasar Iran za ta kulla yarjejeniya tare da kasashen shida, don kawar da damuwar kasashen duniya, dangane da batun nukiliyar kasar ta Iran, idan suka amince da ikon kasar Iran kan mallakar nulikiya.

Ya kuma kara da cewa, idan kasar Amurka na son yin shawarwari kai tsaye tare da kasar Iran yayin wannan taro, kamata ya yi ta amince da ikon hakan, ta kuma tsayar da takunkumin da ta kakabawa kasar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China