in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gabon zata karbi bakuncin babban taron man fetur da nune-nune na Afirka jiko na 5
2013-02-15 19:59:58 cri
Masu shirya babban taron man fetur da nune-nune na Afirka (CAPE V), sun sanar da cewa za'a gudanar da taron a birnin Lebreville na kasar Gabon daga 26 zuwa 28 ga watan Maris.

Kungiyar masu sarrafa albarkatun man fetur ta Afirka (APPA) ce zata shirya taron tare da hadin gwiwar ma'aikatar albarkatun man fetur ta Gabon, inji sanarwar da masu shirya taron suka bayar ranar alhamis din nan.

Babban taron na CAPE V zai kunshi zaman tattaunawa na tsawon kwanaki uku sannan za'a baje koli don nune-nunen kayayyakin albarkatun man fetur da kuma rangadin wasu ayyuka a wannan fanni inji sanarwar.

Taron har ila yau zai samu zuwan jiga jigan wakilai daga sassa na gwamnati da masu zaman kansu daga kasashe wadanda mambobi ne na kungiyar ta APPA da suka kunshi kasashen Aljeriya, Angola, Benin, Kamaru, jamhuriyar Congo, kwadibwa, Jamhuriyar dumokradiyar Congo, Masar, Equitorial Guinea, Gabon, Ghana, Libya, Mauritania, Nijar, Najeriya, Afirka ta Kudu, Sudan da Chadi.

Bugu da kari taron zai samu halartar wakilai daga cibiyoyin kasa da kasa, kamfanonin man fetur, da dai sauran kamfanoni masu harkar man fetur daga nahiyar Afirka.

Sanarwar ta ci gaba da cewa wannan babban taro zai samar da wata muhimmiyar dama, wacce ita ce irinta na farko, ga masu harkar man fetur wadanda suka samu kafuwa da ma wadanda ke neman su fara harka a Afirka. (Lami Ali Mohammed)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China