in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Taron BRICS zai amfanawa Afirka, inji shugaba Zuma
2013-02-15 16:28:32 cri
Burin gwamnatin Afirka ta Kudu na ganin nahiyar Afirka ta cimma inganci a cikin duniya zai samu ci gaba yayin da kasar ta karbi bakuncin taron kasashen BRICS jiko na biyar da za a yi a watan gobe a birnin Durban,in ji shugaba Jacob Zuma, yayin da yake jawabi ga kasa baki daya a majalisar dokokin kasar ran alhamis din nan.

Ya ce suna masu samun kwarin gwiwa dangane da ci gaba da ake samu a fuskar kawance, diplomasiya da kuma tattalin arziki tsakanin Afirka ta Kudu da sauran kasashen kungiyar BRICS.

Wannan suna na BRICS lakabi ne da ake wa kasashe masu tasowa a fuskar tattalin arziki wato, Brazil, Russia, India, Sin, da kuma Afirka ta kudu, wacce zata yi ganawarta jiko na 5 a birnin Durban daga 26 zuwa 27 ga watan Maris.

Haka zalika, shirin kawancen bunkasa nahiyar Afirka (NEPAD) da kuma shirin nazarin kawance a Afirka sunyi bukin cika shekaru 10 da kafuwa.

A matsayinsa na mai kiran taron shuwagabanni karkashin shirin NEPAD, shugaba Zuma yace Afirka ta kudu zata ci gaba da aiki da sauran kasashen don cimma aikin samar da ababan more rayuwa a nahiyar.

Dangane da batun zaman lafiya da tsaro, shugaba Zuma yace za su ci gaba da mara bayan kasar Mali a yunkurinta na tabbatar da ikon kasa.Ya kuma yi kira ga shugabannin kasashen jamhuriyar tsakiyar Afirka, Guinea Bissau, da Somaliya da su ci gaba da aikin tabbatar da zaman lafiya don amfanin jama'arsu.

Ya yi alkawarin cewa Afirka ta Kudu zata ci gaba da mara yunkurin nahiyar Afirka a fuskar tabbatar da zaman lafiya ta hanyar shiga tsakani,ba da gudummawar dakaru da kuma tallafin na kudade da kayan aiki. (Lami Ali Mohammed)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China